part 4

1K 69 0
                                    

🌵🌵🌵🌵
*Koma kan mashekiya*
*(kaikayi)*
🌵🌵🌵🌵

*Labarin wata mata*

*Almost true life story*

Na *Maryam S Indabawa*
*MANS*

🌐 *HAJOW*🌐
🌐🌐🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* 🌐🌐🌐

Page *4*


*Bismillahir Rahamanir Rahim*

*Happy Birthday Anty Rash wish u more years ahead*


Mami ce zaune a falo cikin shiga ta *kasaita.* ta sanya wani farin less wanda a kalla kudin sa zai yi dubu saba'in.

Ta sha kwalliya an zuba gold hannu da wuya da kunne. Gaban ta lemo ne.

Dady ne zaune a gefen ta. Yana sanye da farar shadda ya saka yar ciki da babbar riga.

Dakin sai tashin kamshi yake, Mami ce ta kalle shi ta ce,
"Alhaji kasan abinda kake son ya faru bazai faru ba. Dan *ba dani ba sa lallen kaza.* Ahmad dai ni na haife shi, kuma bazai taba yiyuwa abar shi yayi abinda yake son yayi ba."

Tsaki Dady yayi ya ce,
"Ahmad dan mune gaba daya,  ya kamata ki san lokaci ya canja. Ahmad ba karamin yaro bane da za a tilasta masa auren wacce baya son ya aura. Ya mallaki hankalin kaan sa. Kuma ni da sanin da nai miki yarinyar nan in tazo kina haba haba da ita, kina kaunar ta kwasam yanzu sai naga kin canja. Meyasa?"

Mami ta ce,
"To ai dole ne in canja tinda na riga na jiyo labarin zuri'ar su *Mayu ne,* Matsiya ta yan kauye, bazai taba yiyuwa ba bana kaunar yarinyar nan kwata kwata na *tsane ta.*  bana kaunar *zuri'ar su* kuma bazai taba yiyuwa mu hada zuri'a da su ba *mayu* bazai yiyu ba."

Dady ya ce,
Kinga wannan zargin da kike bashi da asali bare tushe."

"Ai kuwa shi keda asali. Dan dana ya fita turai yai karatu shine wasu *kauyawan* banza zasu so to ce auna so,  *talakawa* dan su tatse shi. A'ah su mallake mun 'da bazai yiyuba wallahi.."
Mami ta fada cikin fada tana dadaga kai.

Wani kallo Dady yake mata dan ba karamin bata masa rai ba.

Dady mutumin kirki ne wanda ya dauki *talaka da me kudi* duk daya.

Ran sa a bace, ya ce,
"wato dai in na fuskan ce ki kina kin auren nan saboda dai *talakawa* ne ko babu *wayewa* tattare dasu kuma basu da *kudi.* Haka ne?"

"Kwarai kuwa haka ne."
Mami ta abashi amsa.

Dady ya ce,
"To in be aure ta ba fada min wa kike son ya aura."

"Haba Alhaji ga yan mata nan barkatai. Idan har baza ka iya zabar masa ba ka bar shi ya huta ya zabi wacce yake so ko kuma ni na zabar masa."

Dady ya ce,
"Kinga kiji *tsoron Allah* a cikin al amuran ki. Saboda tunanin ki ya fara sawa kina wuce *gona da iri*  "

"Hmm!"
Mami taja nimfashi kafin ta ce,
"Kai dai tunanin ka be kai inda nawa yake ba. Dan ni nawa tunanin ya wuce inda kake tunani,"

Kallon ta yayi, ya ce,
"mene amfanin auren yayan masu kudin. Auren yar gidan  mutumci da tarbiyya shi ake kwadayi ba auren abun duniya ba. A abinda zakiyi alfahari da jikokin ki shi zakina hanga."

Mikewa Mami tayi ta kalle shi sama da kasa ta bar wajen.

Kallo ya bita dashi yana girgiza kai.
"Allah ya shirye ki."

Ya fada yana kurbar lemon gaban sa.

Washe gari. Na'ima da Ibrahim na compound din gidan a zaune suna hira wata mota ce ta shigo gida

Koma kan mashekiyya (Back to sender) 2018 (Complete ✔)Where stories live. Discover now