💖💫RUDANI💖💫 70

72 25 96
                                    


**

Da dare fa Ashphert tace bata iya ji ba, ah dawo da Aameer gida with two to three nurse kawae su kula dashi amma ba yanda za'ayi tabar mijinta shi kadai chan ita tana gida hankali kwance "Yanzu hankali kwance kike?" Sabeerah ta tambaya da mamaki dan bata ga alaman kwanciyan hankali tattare da Ashphert ba kuma tana maganan mijinta na chan ita tana nan hankali kwance, shiru Ashphert tayi hakan yasa tace "Muje na sauke ki a gida na wuce kinga dare yi yakeyi, Xeenerh Aameen zai zo ne koh Aa?" Ta tambayi Xeenerh dake gefe tayi shiru, ita damuwan kanta yawa yake dashi, Aameen is not the same human anymore, shi kenan yin dare, wani lokacin ma sai tayi bacci yake dawowa saboda rainin wayo kuma ya fita da sassafe, in banda yau data gansa ah asibiti har ta manta sanda ta gansa da rana, ta masa magana yace aiki, ah gwamnati ne gabadaya "Kuje kawae, koh nan zan kwana" ta fada fuska ba yabo ba fallasa "Toh haka Aameen yace?" Shiru ta mata hakan yasa tace "Zaki bar Affan ya kwana wajen Aunty Nabeelah kenan?" Tace "Eh Yaa Sabeerah, gobe ma tace zata wajen Aameer dan yau sun hana, ya kamata ace sun fara barin mutane suna ganin sa" Ashphert tace "Gaskiya kam dan dazu Aunty Husnah ta kira, itama taje ba'a barta ba" Sabeerah tace "Toh ae ba laifin mu bane, laifin na mijin tane da ya kasa ya tsare Yaa Abu na goya masa baya harda soldiers fa da muka koma dazu na gani, but it's for the good" kallonta kawae sukayi basuyi magana ba "Muje Ash" Ashphert bata ce komai ba ta bita suka fita, zama Xeenerh ta cigaba dayi wajen, ganin baida amfani ta kira Anwaar "Are you out?" Ta tambaya bayan ya dauka "No am home amma yanzu zan fito" tabe baki tayi gane shifa Anwaar bayi yawo sai dare "Can I see you? Ina yanda kabar ni dazu", "Will be right there, but lend me some minutes before that" tace okay, bayan sunyi sallama ta kira Aameen amma da ikon Allah guy innan bai dauka ba, ita haushin kanta ma data kirasa taji, gyarawa tayi ta kwanta kan sofa, bada dadewa ba Anwaar yazo tareda Fadel, ganin Xeenerh ita kadai harta fara bacci yasan sauran ita kadai aka bari, ah hankali ya karasa yayi tapping hanunta, ganin haka Fadel ma ya fara tashin ta, baccin baiyi nisa ba dan dama baso takeyi tayi baccin ba "Yaa Anwaar kazo, Fadel" ta fada tana miqa masa hanu, baiyi rikici ba yaje wajen Xeenerh "Ke kuma mey kikeyi ke kadai nan?" Shiru tayi ma ta rasa yanda zata fara fada masa sanin yau duk bai nutsu ba "Bakomai, dama so nakeyi ka kaini, ban iya night driving ba" kallon wristwatch nasa yayi, ganin 8:56 pm yasan karya Xeenerh keyi "Mey ke damun ki?" Hanun Fadel ta kama tana wasa dashi kafin tace "Akan shine dama" sake kallonta Anwaar yayi, ya gane sarai Aameen take nufi amma yace "Waye shi?" Tace "I mean my husband, Yaa Al'ameen" jin bai amsa ba tacigaba "Yanzu fa bai dawowa sai chan dare wani lokacin sai nayi bacci, kuma da safe yake fita, kuma har waya da safe da dare duk yi yakeyi" shiru kawae Anwaar yayi jin yanda take bayani, su fa mata matsalan su kadan ne, zai iya cewa ma basuda matsala, banda haka shi fa bai ga laifin abun ba amma ita har tayi figuring "Aure zai sake?" Ya tambaya "Thank you very much, dama abunda nakeso ka gane kenan ashe kuma ka gane" murmushi yayi kawae "Ba ganewa nayi ba, nasan dai abunda kikeso ki fada kenan right?" Tace "Tunda dai ka gane ae shikenan" ta fada tana bata rai "Toh meyasa baki so ya sake aure?" Yanzu fa ta gane shi Anwaar mugun dan rainin wayo ne, gyara Fadel da ya fara bacci tayi bata amsa Anwaar ba "Xeenerh I asked you something" Xeenerh kaman tayi kuka "I can see how Ilhaam is suffering, I can't risk my life too" at this moment Xeenerh ta bashi dariya sosai amma ya daure baiyi ba "Ina cutar da Ilhaam kenan?" Ya sake mata wani tambayan, girgiza kai tayi "Ni bance ba, amma she is always crying ae" ta fada dan ta rasa abun fada, ita fa Ilhaam bata cewa Xeenerh batajin dadin rayuwanta ba kawae dai hakan Xeenerh ke gani, ita gani take duk mey kishiya farincikin ta bai da yawa "Let's just forget about this Yaa Anwaar, we have many things to deal with, kawae dai inasan sanin matsalan Yaa Al'ameen" yace "Aiki ne fa kawae ya masa yawa Xeenerh, I don't know him with any other girl" ya kwantar mata da hankali kuma gaskiya ne "I am feeling insecure, as you all are going back in good terms to your exes, hakan shima yakeso yayi?" Anwaar yace "There's nothing wrong in that but believe me Al'ameen will not be included" shiru tayi kafin tace "Am I his first love?" Murmushi yayi gane Xeenerh nason ya fadi abunda yafi karfin sa "Yea, you are" ya mata karya, zaiyi wuya ae daman ace Xeenerh itace Aameen's first love, bai zauna da ita sosai ba balle ma, he dated one girl yanzu kuma tayi aure kuma bata zaune anan ma, ba yanda za'ayi su sake haduwa da yardan Allah, kuma koh sun hadu yarinyan batada matsala koh kadan, all that explanations aside, yasan confirm Xeenerh dated someone before Aameen, toh ae ba matsala bane duk wannan, sai wanda Allah yayi zaka aura kafin ka aura, ganin how she looks happy shima yayi murmushi ganin an wuce wajen "I will make sure I talk to him, yanzu ki tashi na kaiki gida" tace "Okay, thank you so much, na tafi da Fadel?" Ta fada tana kokarin tashi "Call Ilhaam and explain yourself, tace akai mata Fadel, yanzu wajenta zamu" Xeenerh awwn "Ban jin neman fada yau da na tafi dashi ae sai tayi fadan ta" murmushi kadai Anwaar yayi, yasan Ilhaam na zaune na jiran Fadel, at the other hand yasan gobe Fatima zata kaishi gidan su, shi baisan meyasa batasan yaronta wajen Ilhaam ba, yasan kuma inda Ilhaam ne ta haifi Fadel bazata hana yana zuwan wajen Fatima ba, two different humans.



💖💫RUDANI💖💫Where stories live. Discover now