💖💫RUDANI💖💫 86

48 25 63
                                    


Here comes a several-month leap. Teemerh na zaune ita kadai tana kallo dan har lokacin tana gida Anwaar bai sake bin ta kanta ba, yasan batayi hankali ba koh ba'a fada masa ba, abu guda daya dai kawae yace bazai rabata da Fadel ba tunda ita ta haifesa, Fadel need his mother, kuma shi baida wata matan ah gida, koh Munnirah mey kulawa da Fadel yanzu tana wajen Ummi, and Ilhaam's obsession with Fadel yanzu da sauki dan ba kullum take ganin sa ba. Ita kuma Teemerh har Ilhaam ta kira tace ta tayata ba Anwaar haquri amma Anwaar shiru "Yanzu Fatima ashe Ilhaam ciki takeda shine baki fadamun ba?" Mummy ta zauna kusa da ita tana tambaya, shiru ta mata dan tun bayan dawowanta gidan shirin su da sauki, abunda ta tabbatar Mummy ta mata shine rokan Daddy da suka hadu harda Yaa Xee tazo sukayi wae ya yabar Teemerh ta zauna, saida ya kusan 6ata musu rai kafin ya yarda ta zauna mishi a gida, saidai yanda Daddy yake sama-sama da ita haka take da Mummy, abun bai baci ba saida tagano one of Mummy's darkest secret, ita ta kashe Mami and framed Ummi in it saboda sunanta kar ya fito, ita batasan laifi koh kadan, sure Mummy is one of the selfish people "Ba magana nake miki ba?" Gyad'a kai tayi "Eh tanada ciki, farin ciki ya kamata tayi ae" ta fada sannan ta maida kanta gun Tv "Yanzu Ilhaam ce kikeso tayi farin ciki?" Mummy ta tambaya da mamaki "Komai Ilhaam, yanzu watana nawa ah gida Mummy? Amma dukda haka ba neman hanyan dazan koma kikeyi ba, duk fa dalilin Ilhaam Anwaar yace na dawo gida, koma kikeso na sake aikata wani kuskuren?" Zata sake magana Teemerh ta katse ta "I know you killed Mami, she was your friend Mummy, amma ke baki rage mata ba, Aameer shi ke kulawa da case in, shima baki rage masa ba, you tried to kill him months ago and we kept on blaming Ahmad for your mistakes. Tell me your enmity with the Albaaz family Mummy, if only I can testify against you in court then I will surely d-" daga ido Teemerh tayi ganin waye ya mareta, Aunty Shamsiyya ne tsaye da rubber silicone ankle nata dan ba wanda zaiyi zaton ba nata bane ma, tafiya takeyi tsaf dashi har yawo tanayi dan color'n yayi matching da skin nata, ta karaso taji Teemerh nakan siding Family'n mijinta, toh shine dalilin marin, har Teemerh zatayi dariya ta fasa ganin wae Aunty Sham ke yawo da finger counter tana Tasbihi ne koh Istighfar takeyi oho "Gaskiya ae na fada, wae fa ah haka Anwaar baisan duk laifin da nayi ba, ae da abun sai yafi haka" ta fada kaman mey shirin kuka "Ohh yanzu wae saboda wata banza da bama matarsa ba ya miki wancan dukan kwanakin?" Tashi Teemerh tayi dan ba cigaba da jin su zatayi ba. Tana tashi ma Amrah ta mata waya tana hanya, daki ta wuce ta kwanta dan jiran Amrah yanda baza'a dameta da wasu maganganun Ilhaam ba, tana ita kadai Habeey tayi sallama Amrah a bayanta hakan yasa ta tashi ta zauna "Ga Amrah" ta fada sannan ta juya ta fita leaving Teemerh and Amrah "Teemerh ina Fadel kam?" Teemerh tace "Yana wajen Daddy, ae in kin gansa anan toh Daddy bayi nan" kallonta Munnirah ta sake ganin yanda idonta ya kumbura kullum kuka toh "Why not ki fada ma Anwaar duk abunda kikayi as you told me the other day? Kinga da lokaci guda zai yi fushi ya bari, amma yanzu kinyi wannan daban, in ya sake jin wasu abunda kikayi wlh zaiyi abunda yafi wanda ya miki last time" shiru Teemerh tayi kawae tana jin Amrah, saida ta gama tace "Amrah wlh kusan kullum Anwaar sai yazo wajen Fadel, amma innace miki na tab'a maganan 10mins dashi na miki karya, na yarda cewan I've taken things too far, amma ya kasa gane cewan I regretted my actions" ta fada dan siririn hawaye na bin fuskan ta, saurin girgiza kai Amrah tayi "Wlh bakiyi regretting komai ba Teemerh" kallon mamaki Teemerh ta bita dashi ta fara share hawayen "Eh nasan abunda nake fada, cewa nayi bakiyi regretting komai ba. Kina san sanin dalilina na fadin haka?" Daga kai tayi ah hankali "Kefa kawae gani kike zaki rasa Anwaar shiyasa kike ganin ya dace ki bada haquri ki koma dakin ki, am very sure inda zaki koma, itama Ilhaam a maida auren su tsaf sai kin sake yin wani abun, kin shiryu ne saboda kin gano Anwaar bazai yi tolerating muguntan da kikewa Ilhaam ba. Teemerh ki shiryu saboda Allah koda zaki rasa Anwaar" saurin girgiza kai tayi "Wlh Amrah na shiryu, na kira Ilhaam na bata haquri" kallonta Amrah tayi ta girgiza kai "Baki jin magana, yace ba ruwan ki dasa Ilhaam cikin maganan miye na kiranta? Wlh ba kiyi hankali ba tunda keda mijin ki baza kiyi abunda zai yafe miki da kansa ba sai kin sako wata, kema matan sane ya kamata ki koyi yanda ake bada haquri wa miji ba sai kin sako wata ba, dama tun farko kinsa ah ranki ta fiki, dole kiyi ta ganin haka" sake gyara zama Teemerh tayi tana kallonta "Meyasa? Yana jin maganan ta, dole na fada mata ta basa haquri" tsaki Amrah tayi dan ba karamin takaici Teemerh ke tara mata ba "You are his wife, kuma dalilin da yasa yace kar ki fada mata ae saboda keda shi abun ya shafa, in laifi ta masa ke jin nata kikeyi? Teemerh kina bani haushi. Kince kusan kullum sai yazo and still sai kin jira wata ta basa haquri? Ita Habeey mey takeyi da baza ku hadu ku basa haqurin ba? Kullum sai yazo, da ace kullum kike basa haqurin dole ya haqura koh shi ya kawo iskanci duniya" Amrah ta fara masifa dan Teemerh ta bala'in bata mata rai "Amrah am afraid na fada masa sauran abunda nayi zai tsane ni har abada, har wajen boka fa ina zuwa, kuma ga na Ahmad, am finished" ta daura hanu akai kafin ah hankali ta cire, Amrah hummed, dan abubuwan da Teemerh tayi koh itane ba yafe mata zatayi ba, magana na Allah kenan "Teemerh kina manta kinsa anyi raping Ilhaam koh?" Shiru Teemerh tayi dan ba mantawa take ba tunawa ne batasan yi "Nasani Amrah, ban manta ba" ta amsa "Tsakani da Allah Teemerh kinsan dai in ba Anwaar ba wlh koh Ahmad ba aurenta zai ba, haba you cheated her" shiru Teemerh tayi dan ita ba damuwan ta a zauna ana tuna mata ba, kawae Anwaar yayi haquri ta koma dakinta tunda da aurensa kanta "Gashi" ta bata katin auren da ta kawo mata, hanu tasa ta karba ta ajiye gefe dan koh dubawa batayi ba, tana san zuwa dan yanzu bata wani fita amma tsoro take tunda bata tambayi Anwaar ba, ya ganta zai kara yarda ba hankali tayi ba gwanda ta haqura "Zaki zo?" Girgiza kai tayi dan zaiyi wuya "Maybe, koh Daddy ba bari zaiyi na fita ba" dariya Amrah ta fara kaman ta tuna wani abu "Allah Anwaar baida kunya, yanzu ya ajiye ki gidan naku kuma yana zuwa Daddy na ganin sa amma koh kunyan sa bazai ji yace ki koma ba?" Teemerh tace "Ae Daddy ke daure masa, yace yayi daidai" shiru Amrah tayi jin haka "Allah ya kawo sauki toh zan tafi" saurin rike ta Teemerh tayi "What was Ahmad's excuse to be using women? He used me too and I told you, the saddest thing da aurena Amrah, Ahmad is really a beast" Amrah tace "Mey kikeso nace Teemerh? Ke kika ja komai wa kanki, ya gane bakiso asirin ki ya tonu shiyasa ya miki abunda ya miki, da kin gwada masa baki damu ba wlh da ya shiga hankalin sa" shiru tayi ganin Teemerh na kallonta kafin ta cigaba "Yayi alqawarin yiwa mata abunda yaso saboda Daddy'n mu ya cuci Mama. That was not an excuse amma matan ke biye masa" tabe baki Teemerh tayi tana tunanin da wanne zata fara, ita laifin ta da yawa.




💖💫RUDANI💖💫Where stories live. Discover now