14

4.5K 248 8
                                    

_*RABO AJALI...!*_

*HAUWA A USMAN*
_JIDDARH_

'''Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh'''

*MASU SIYAR MIN DA NOVELS ALLAH YA ISA BAN YAFE BA*

*ZAN CIGABA DA YIN POSTING RABO AJALI IN SHA ALLAH, AMMA MATUK'AR AKA CIGABA DA SIYAR MIN DA NOVELS CIKI ABU HUD'U TABBAS ZANYI D'AYA, KO NA MAYAR DA NOVELS D'INA NA KUD'I, KO NA YI APPLICATION NA MAYAR DA NOVELS D'INA CIKI, DUK MAISO YAJE PLAY STORE YAYI DOWNLOADING KO NA MAYAR KAN YOUTUBE DUK MAISO YAJE CAN YA SAURARA, KO NA DAINA RUBUTUN KWATA-KWATA GABA D'AYA DAN BAI YIWA KURA DA SHAN BUGU GARDI DA KWACE KUD'I, NI INA NAN INA SHAN WAHALA WANI NA CAN NA AMFANI DA WAHALA TA, BASIRA TA BA*

'''DEDICATED TO'''
*ZUWAIRAT UMMU MARYAM*

1⃣4⃣

Cikin zafin rai Neehal yace " wannan itace kalma ta farko da zaki fara yi min magana da ita.....!?

" Baki tambaye ni ya nake ba, baki tambaye ni lafiya ta da inda nake ba...!,
sai wani zancen banza kika fara yi min, good yayi kyau!,
saboda nayi waya dake ko bacci kirki banyi ba, & saida nayi tafiyar 4km,
amma shine kika yi min wannan tarbar ko....!?

"Baki tambaye ni duk abinda ya shafi lafiya da rayuwa ta ba,
babu tambayar yanayi ko halin danake ciki, saboda lafiyata da rayuwa ta basu dame ki ba,
sai zancen mace bayan kin san matuk'ar lafiyar Allah babu yadda za'ayi na d'auki lokaci haka banyi waya dake ba,
to hell with you Najwah, dakyar Najwah tayi k'ok'arin saita nutsuwarta,
tace " kayi hak'uri wallahi munanan mafarkai nake tayi ne,
" to da kike ta munayen mafarkai abinda ya kamata kiyi min yanzu kenan.....!?

"Ko ke a ganinki ta wannan hanyar ya kamata ace kin tarbeni....!?

" Ai da kike mugayen mafarkan ne ma ya kamata ki tambaye ni lafiya ta,
ya kuma kamata ki tsaya kiji abinda zance miki, amma dayake jahilin kishin ya gama rufe miki ido,
bama ki tsaya kin saurari halin danake ciki ba, balle ki tsaya kiji abinda zance miki,
imma a cikin wani yanayi ko mugun hali nake duk bai dame ki ba,
saboda rayuwata da lafiya duk basu shafe ki ba, basa kuma gabanki,
yayi maganar da d'an zafi, cikin matsanancin kuka har muryarta na shak'ewa,
tace " mafarki nayi kana rayuwa da wata mace,
yadda kasan rugugin saukar aradu haka k'irjin Neehal yayi muguwar bugawa da tsananin k'arfin gaske,
cikin rawar murya da d'an fad'a yayi k'arfin halin cewa " saboda ni fasik'i ne kuma  mazinaci ne ko....!?

"Saboda ni babu abinda ke gaba na sai mata......!
wai ni tsaya ma dan Allah Najwah me kike d'auka ni ne....!?

"Wanne irin kallo kike min.....!?

" A layin wad'anne irin mutune kika aje ni, mazinaci, ko fasik'i ko mutumin banza ko me......?

Ya k'arasa maganar muryarshi na cracking, cikin muryar kuka tace " Allah ko d'aya bana yi maka kallan d'aya daga ciki,
kawai hankalina ne yak'i kwanciya, nutsuwata tak'i barina na samu salama,
tunane-tunane sunyiwa zuciyata yawa, kullum cikin tunani nake,
saboda jiki na yana bani abubuwa da dama,
ko nayi k'ok'arin k'aryata zuciyata da abinda jikina yake bani,
bana iyawa na rasa meyasa, but am sorry,
" saboda abinda kika sakawa ranki kenan, shiyasa kika k'i kyale kanki zama lafiya,
cikin lumana da kwanciyar hankali, ke kullum kina cikin yi min mummunan zato,
baki tab'a kyautata min zato na rasa dalili,
kuma abun yana matuk'ar damuna ace matata ta sunna itake yi min wani irin kallo,
itake zarginna, tak'i kyautata min zato, a zahirin gaskiya idan nace miki ban jin haushi nayi miki k'arya,
dan abun yana matuk'ar damu na, yana k'ona min rai na,
ke baki bar kanki kin samu nutsuwar ruhi da salama a zuciyarki ba,
nima baki barni ba, gaskiya ki canja, yayi maganar cikin k'arfin hali,
" to amma dai ai na baka hak'uri ko....!?

RABO AJALI...!حيث تعيش القصص. اكتشف الآن