19

1.3K 172 126
                                    

RAYUWA DA GIƁI  19


Batul Mamman💖




***

Bayan sallar asuba Taj ya kira Kamal domin su yi sallama. Jiya basu sami haɗuwa a gida ba. Ya yi ta waya shiru Kamal ɗin bai ɗauka ba. Wanka ya yi ya gama shiri da sauri ya sake duba wayar. Abin mamaki Kamal bai bi kiran nasa ba. Da wahala hakan ke faruwa. Jikinsa sai ya bashi ko ba ƙalau ba. Abba ƙaninsa ya kira ko tunawa da lokaci bai yi ba.

"Happiness ya fito sallar asuba kuwa?"

Abba ya ɗan wartsake idanu "ya fito amma yau ya riga kowa baro masallacin. Saƙo ne?"

"Ɗan leƙa min shi please."

Abba baya son fita don bacci ne sosai a idonsa ya ce "Ya Taj ya dai kamata ku rage wayar asubar nan. Kai kayi aure, idan shi ma ya yi wallahi za ku dinga samun matsala da matanku."

"Za ka tashi ko kuwa?" Taj ya ɗan ɗaga murya da ƙoƙarinsa na ɓoye yadda ya damu.

Yana jin ƙunƙunin Abba har ya isa ƙofar ɗakin Kamal. Sallama ya haɗa da ƙwanƙwasawa.

Da ƙyar Kamal ya iya buɗe jajayen idanunsa da su ka kumbura kamar wanda ya kwana yana kuka. Jikinsa gabaɗaya ciwo yake yi. Kansa kamar ana sara guduma saboda azabar ciwo.

"Waye?" Muryarsa ta fito a dusashe.

"Ya Taj ke nemanka." Abba ya faɗa yana saita bakinsa da ƙofar yadda za a ji da kyau "na sanar dashi. Can I go back to bed now?"

"Thanks" Taj ya ce da kulawa.

Wayar Kamal ya sake nema. Yadda yaji muryarsa ya tayar masa da hankali. Amma Kamal ɗin ya tabbatar masa da mura ce ta kama shi da zazzaɓi.

"Allah Ya ƙara sauƙi. Ko na bar tafiyar yau muje asibiti?" Hamdi ce ta faɗo masa ya yi murmushi.

"Ka tafi kafin Amma ta sauka a garin nan duk mu shiga tara."

"Don Allah ka je asibiti dai. Bana so ana raina mura da zazzaɓi. Ciwukan gaske ne."

"To doctor." Kamal ya zolaye shi.

Suna gama wayar ya ɗauki ƴar jakarsa ta goyo (backpack) wadda ya sanya duka abubuwan buƙatarsa a ciki. Ƙananan kaya ya saka ya koma matashi sosai. Haramar tafiya ya yi sai ya tuna yadda Kamal ya damu kada Ahmad yaji babu daɗi akan halin da Salwa ke ciki. Lokaci ya duba akwai đan saura. Ya fito falo ya kira wayar Ahmad ɗin.

"Yaya na shirya zan tafi."

Ahmad ya miƙe da sauri. Dama bai koma bacci ba tun sallar asuba.

"Bari na zo na kai ka airport."

"Ka barshi. Zan sami adaidaita sahu."

Fitowa Ahmad ɗin ya yi. Su ka gaisa sannan ya miƙa masa key ɗin motar Kamal.

"Incase ban sami dawowa akan lokaci ba, ina sa rai jibi motata za ta iso. In bawa mutumin numbarka sai ya kawota nan ya ajiye?"

"Da ina zai kai?" Cewar Ahmad yana zura muƙullin a aljihun wando.

Zama Taj ya yi ya buƙaci yin magana da shi na mintuna kaɗan.

"Yaya akan Salwa ne."

Ahmad ya ɗan ɓata rai "ka cire lamarin yarinyar nan daga gabanka ka fuskanci matsalolinka."

"A'a Yaya. Idan da kara nima ƙanwata ce. Ba kuma zan so ta shiga irin wannan yanayin akan wani ba."

"Shin ka taɓa yi mata magana ko nuna mata alamun soyayya ne?"

Ya kaɗa kai da sauri "a'a."

"To ka gani. Rigima ce kawai irin ta ta. Tun abin nata bai yi nisa ba na bata shawara taƙi ji. Ya take so ayi mata? Ana forcing soyayya ne?"

RAYUWA DA GIƁIWhere stories live. Discover now